1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

'Yan jarida sun lashe kyautar Nobel ta bana

October 8, 2021

An karrama 'yan jarida biyu saboda kwazonsu wajen kare 'yancin aikin jarida da ma na fadin albarkacin baki, kamar yadda kwamitin bayar da yabon na Nobel ya fada.

https://p.dw.com/p/41RUv
Bildkombo-Die Freidensnobel-Preistraeger Maria Ressa und Dmitry Muratov 2021

An bayyana wata 'yar jaridar kasar Philippines, Maria Ressa da kuma Dmitry Muratov dan kasar Rasha, a matsayin wadanda suka lashe kyautar Nobel a bana.

An karrama 'yan jaridar biyu ne saboda kwazonsu wajen kare 'yancin aikin jarida da ma na fadin albarkacin baki.

Maria Ressa dai na aiki ne a matsayin shugabar wata jaridar Intanet da ke binciken kwa-kwaf da ake kira Rappler, yayin da shi kuwa Dmitry Muratov ke matsayin babban editan jaridar Independent a Rasha.

Kwamitin bayar da lambar yabon ta Nobel a kasar Norway, ya ce mutanen biyu hazikai ne da suka cancanci karramawa a wannan zamani da aikin jarida da tsarin dimukuradiyya ke fama da matsaloli.

Akalla dai 'yan jaridar za su samu kudaden da za su kai euro dubu 985.