1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Burkina Faso: Yan bindiga sun kashe fararen hula

Ramatu Garba Baba
May 20, 2023

Fararen hula kimanin 12 ake zargin wasu mayaka masu da'awar jihadi da kashewa a wani hari da suka kai a yankin yammacin kasar Burkina Faso.

https://p.dw.com/p/4RcKT
Mutum sama da 30 'yan bindiga suka kashe a wannan makon a Burkina Faso
Mutum sama da 30 'yan bindiga suka kashe a wannan makon a Burkina FasoHoto: BURKINA FASO'S PRESIDENTIAL PRESS SERVICE/REUTERS

A kasar Burkina Faso da ke yankin Sahel, fararen hula kimanin goma sha biyu ake zargin wasu mayaka masu da'awar jihadi da kashewa a wani hari da suka kai a yankin yammacin kasar da ke iyaka da kasar Mali.

Wani ma'aikacin gwamnati da ya nemi a sakaya sunansa ya ce, maharan sun zo da yawansu dauke da muggan makamai, sun afka wa kauyen mai suna Kie a daren Jumma'ar da ta gabata, in da suka yi wa kauyen kawanya kafin daga bisani sun cinna masa wuta, da wuya a iya tantance adadin mutanen da ya ce, an kashe ganin da yawa sun ji munanan rauni baya ga asarar dukiyar da aka tafka a harin.

Kazamin harin na zuwa ne, kwana guda bayan wani makamancinsa da 'yan bindiga suka kai da ya salwantar da rayuka ashirin a kasar da yanzu haka ke fada da ayyukan 'yan ta'adda.