1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaTurai

WikiLeaks: Assange ya yi nasara ta wucin gadi kan Amurka

March 26, 2024

Kotun Birtaniya ta bukaci Amirka da ta bada tabbacin kare lafiyar mawallafin jaridar WikiLeaks Julian Assange da Washington ke zargi da fallasa bayanan sirin kasarta.

https://p.dw.com/p/4e9Vf
Matar mamallakin jaridar Wikkileaks Stella Assange a yayin zaman kotun Burtaniya
Matar mamallakin jaridar Wikkileaks Stella Assange a yayin zaman kotun Burtaniya Hoto: Toby Melville/REUTERS

Babbar kotun ta ce wajibi a Amirka ta tattabar cewa ba za ta yanke masa hukuncin kisa ba idan aka mikashi  domin fuskantar hukunci.

Karin Bayani: Assange ya yi nasarar daukaka kara 

An dai shafe kusan shekaru 10 ana kai ruwa rana kan shari'ar, Assange wanda a yanzu yake da shekaru shekaru 52 yana fuskantar tuhume-ruhume 18 dangane da cin amanar kasa bayan da ya wallafa bayanan sirrin sojin Amirka a kasashen Iraki da Afhanistan.

Karin Bayani: Za a cigaba da shari'ar Assange a Birtaniya 

An fara sanin shafin na WikiLeaks kusan shekaru 13 da suka gabata bayan ya bankado labarin wani jirgin shelikwaftar Amurka da ya hallaka mutane da dama a birnin Bagadaza na kasar Iraqi ciki har da ma'aikatan kamfanin dillancin labarai na Reuters. Julian Assange ya shafe lokaci mai tsawo a cikin ofishin jakadancin Ecuador a Burtaniya.