1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Corona za ta wahalar da wasu kasashen Afirka

April 9, 2020

Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO, ta yi gargadin cewa nan da 'yan makonni masu zuwa adadin masu Coronavirus zai karu a kasashen Afirka, tana mai jaddada bukatar samar da kayan gwaji a nahiyar da gaggawa. 

https://p.dw.com/p/3aj3H
Südafrika Coronavirus Handschuhausgabe
Hoto: picture-alliance/AP Photo/T. Hadebe

Michel Yao, babban jami'in WHO a Afirka shi ne ya yi wannan gargadin a ranar Alhamis, yana mai cewa idan har aka ci gaba da tafiya a irin yadda ake a yanzu to Afirka za ta samu yawaitar annobar Coronavirus kamar yadda ake gani a kasar China da nahiyar Turai. Sai dai bai bayyana sunayen kasashen da za a samu yawaitar annobar ba.

Kawo wannan lokaci kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ce akwai kusan mutum 11,000 da ke da cutar Corona a Afirka, cutar ta kuma yi ajalin mutum 562 a kasashen Afirka.