1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Wata Kotu a Masar ta yanke hukunci a kan wasu ' yan ƙasashen waje.

June 4, 2013

Masu fafutukar kare hakin demokraɗiya 43 ne, waɗanda ake zargin ba su da izinin gudanar da ayyukansu kotun ta hukunta. A ciki har da wata ƙungiya ta Jamus wato Konrand Adenauer .

https://p.dw.com/p/18jb5
epa03045312 The entrance of the building of Konrad Adenauer Foundation which was raided by the Egyptian authories on 29 December, in Cairo, Egypt, 30 December 2011. Egyptian authorities raided the offices of about 17 rights groups and non-governmental organizations, including rooms of the German Konrad-Adenauer-Foundation, which is linked to the conservative party of German Chancellor Angela Merkel. EPA/KHALED ELFIQI +++(c) dpa - Bildfunk+++
Hoto: picture-alliance/dpa

Wata kotu a birnin Alƙahira na ƙasar Masar ta zartar da hukuncin ɗaurin shekaru ɗaya zuwa biyar ga wasu gungun wakilai na ƙungiyoyin masu zaman kansu 43 waɗanda ta ke tuhuma da gudanar da ayyuka ba bisa ƙaida ba, ta hanyar samar da kuɗaɗen haram. Daga cikin mutanen guda 43 da aka yanke wa hukunci, 27 an yanke masu hukuncin ɗaurin shekaru biyar kana wasu 16 aka yanke masu hukuncin ɗaurin shekaru biyu ciki har da wani Ba'amirke.

An gabatar da mutanen ne a gaban Kotun, tun a shekara ta 2012 bayan binciken da aka gudanar a kan ƙungiyoyin da suke jagoranta waɗanda suka haɗa da Konrad Adenauer ta Jamus da NDI National democratic Institue ta Amirka.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Saleh Umar Saleh