1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Wani sabon rikicin ƙabilanci ya ɓarke a Darfur

June 25, 2013

An kashe mutane aƙalla 80 tun daga farkon watan Mayu a faɗan da ake gwabzawa tsakanin wasu ƙabilu biyu da ke Darfur a ƙasar Sudan

https://p.dw.com/p/18wXw
Some of the 300 fighters of the Justice and Equality (JEM) Movement wait to greet Sudanese presidential adviser Nafie Ali Nafie during his visit to al-Fasher, Northern Darfur, on July 25, 2011. AFP PHOTO/ASHRAF SHAZLY (Photo credit should read ASHRAF SHAZLY/AFP/Getty Images)
Hoto: Getty Images

Ƙabilun na Gimir da Beni Halba na kabsa faɗa ne tun cikin watan Afrilun da ya gabata a garin Edd-Al-Fursan a kan rigingimu gonaki da filaye.

A farkon watan Mayu aƙalla mutane 80 suka mutu a faɗan wanda masu aiko da rahotannin suka ce an ƙone gidaje da dama. Ƙwararrun a kan sha'anin kare hakin hakin jama'a na MDD sun zargi gwamnatin Sudan da ƙara rurra wutar rikicin tsakanin ƙabilin biyu. Shugaban rundunar wanzar da zaman lafiya na MDD Ibn Chambas ya ce faɗan ya tilastawa mutane kamar dubu ɗari uku barin gidajensu tun daga farkon wannan shekara kawo yanzu.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Usman Shehu Usman