1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaSudan

UNHCR na bukatar kudade saboda Sudan

September 4, 2023

Sakamakon karuwar yanayi na jinkai a Sudan, Majalisar Dinkin Duniya na neman kudaden da suka zarta bukatar da gabatar domin ceto miliyoyin 'yan kasar da yaki ya daidaita.

https://p.dw.com/p/4VwLL
Hoto: ZOHRA BENSEMRA/REUTERS

Majalisar Dinkin Duniya ta ce tana bukatar dala bilian daya domin kai agajin gaggawa ga mutane kusan miliyan biyu da ke kokarin gudun hijira a Sudan.

A bayanin da ta yi game da wannan batun, hukumar kula da 'yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniyar UNHCR ta ce kudaden da take son samu a wannan karon sun ninka har sau biyu daga adadin bukatar da ta gabatar a watan Mayu.

Miliyoyin 'yan kasar Sudan ne dai ke kokarin tserewa daga yakin basasar da ake gwabzawa tsakanin sojojin da ke gaba da juna a kasar, lamarin da ya haddasa mutuwar dubban mutane, ko baya ga masu kokarin hijirar guje wa halin da ake ciki a kasar.