1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaTurai

Rasha ta tsagaita wuta a birnin Mariupol na Ukraine

April 25, 2022

Sanarwar Rashan ta wannan Litinin ta ce ta yi haka ne domin bayar da dama a kwashe fararen hular da ke zaune kusa da kamfanin a wannan gari mai teku da Ukraine da Rasha suka kwashe makonni suna ''tata-burza' da makamai.

https://p.dw.com/p/4APQE
Ukraine-Konflikt, Eindrücke aus Mariupol
Hoto: Peter Kovalev/TASS/dpa/picture alliance

Dakarun Rasha sun sanar da tsagaita wuta a kusa da wani kamfanin sarrafa karafa na birnin Mariupol a Ukraine. Sai dai kuma, a wasu yankuna na Ukraine, ana zargin Rasha ta kaddamar da hare-hare kan tashoshin jiragen kasa.

Wannan na zuwa ne a yayin da ma'aikatar harkokin wajen Rasha ta musanta yunkuri na gudanar da kuri'ar jin ra'ayin jama'a domin karbe iko da yankin Kherson na kudancin Ukraine. A ranar Jumma'ar da ta gabata ce dai Shugaba Volodymyr Zelenskyyna Ukraine ya zargi mahukuntan Moscow da wannan kokari.