1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana son Taliban ta mutunta mata

Ramatu Garba Baba
August 18, 2021

Amirka da Kungiyar tarayyar Turai da kuma wasu kasashen duniya akalla 18 ne suka yi kira ga Taliban kan mahimmancin mutunta 'yancin mata da yara kanana.

https://p.dw.com/p/3z80j
Afghanistan | Kinderklinik in Dand
Hoto: Elise Blanchard/AFP

A sanarwar hadin gwiwa da suka sanya ma hannu a wannan Laraba, sun yi kira ga Taliban kan ta inganta rayuwar wadanda ake wa kallon mafi rauni a cikin al'umma, ta hanyar ba su damar yin aiki da bidar ilimi da kuma ba su gwargwadon 'yancin walwala.

Kiran da suka yi baya rasa nasaba da zargin tauye 'yancin mata da yara da aka zargi Kungiyar Taliban da yi a lokacin mulkinta kafin a hambarar da gwamnatin kungiyar. Sun kuma baiyana damuwarsu a game da hali na rashin tabbas da rayuwar mata da kuma kananan yara za su kasance a halin da kasar ta Afghanistan ta tsinci kanta a yanzu.

A daya bangaren kuwa, wani sabon rahoto daga kasar ta Afghanistan, na cewa mutum uku sun mutu wasu shida sun ji rauni, a yayin da Taliban ta yi kokarin tarwatsa dandanzon masu zanga-zanga da kwace ikon da ta yi a yankin gabashin kasar. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da shugabanin Kungiyar Taliban da suka yi gudun hijira, suka soma komawa kasar don shirin kafa gwamnati.