1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kamen masu taya Maroko murna a Turai

Binta Aliyu Zurmi
December 11, 2022

An kama daruruwan magoya bayan tawagar kwallon kafar kasar Maroko a manyan biranen kasashen Turai, bayan da murnan nasarar da Maroko ta yi ta rikide zuwa rikici a tsakaninsu da jami'an tsaro.

https://p.dw.com/p/4Knjs
Belgien Brüssel | Unruhen nach WM Spiel - Fans von Marokko
Hoto: Nicolas Maeterlinck/BELGA/dpa/picture alliance

A birnin Paris jami'an tsaro sun tabbatar da tsare mutane 108, inda suka ce sama da mutane dubu 20 ne suka yi tattaki a dandalin Champ-Elysees. Jami'an tsaro sun ce magoya bayan Marokon sun harba musu tartsatsin wuta, yayin da suke kokarin dakatar da su. A biranen Amsterdam da Rotterdam da kuma Utrecht na kasar Holland kuwa, bayan kame wasu mutanen jami'an tsaro sun tabbatar da mayar da doka da oda. A Brussels babban birnin Belgium ma sama da mutane 60 aka tabbatar da damkewa, yayin da a birnin Milan na Italiya aka dabawa wani mutum dan arewacin Afirka wuka a wuya a lokacin bikin nasarar ta Maroko.