1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tura ta kai bango a Siriya

July 27, 2012

A na ci gaba da yin bata kashi tsakanin dakarun gwamnati da na 'yan tawaye a garin Alepo birnin na biyu mafi girma na Siriya

https://p.dw.com/p/15fCj
A fire burns after a shelling at Tafes near Deraa July 22, 2012. Picture taken July 22, 2012. REUTERS/Shaam News Network/Handout (SYRIA - Tags: POLITICS CIVIL UNREST CONFLICT) FOR EDITORIAL USE ONLY. NOT FOR SALE FOR MARKETING OR ADVERTISING CAMPAIGNS. THIS IMAGE HAS BEEN SUPPLIED BY A THIRD PARTY. IT IS DISTRIBUTED, EXACTLY AS RECEIVED BY REUTERS, AS A SERVICE TO CLIENTS
Hoto: Reuters

Rahotannin daga Siriya na cewar dakarun gwamnatin Bashar Al Assad sun sake kai wani farmaki  na  ruwan bama bamai ta jiragen sama masu saukar ungula da jijifi a birnin Alepo birnin na biyu mafi girama´na ƙasar.

Wani ɗan adawar ya shaida wa kamfanin dilancin labarai na Faransa AFP cewar ya ga tankokin yaƙi kusan guda ɗari da suka shigo birnin na Alepo. Amurka ta baiyana fargabanta akan yiwar aikata kisan kiyasu na sojjin gwamnatin akan farar hula a unguwanin birnin da galibi yan tawaye suka yi shelar iko da su. masu aiko da rahotanin sun  ce jama'a maza da mata da yara na ta tsrewa daga yanki a cikin manyan motoci gabannin bata kashin; ta ɗaukar ma  rai ,da ake shirin yin tsakanin sasan biyu masu gaba da juna.

A halin da ake ciki kuma wasu rahotanin na cewar wata yar majalisar dokokin daga garin Alepo,Ilkas Al Badaoui ta canza sheƙa domin bin bayan sahun yan adawa kuma ma har  ta tsallaka zuwa ƙasar Turkiya.

Mawallafi: Abdourahamane Hassane

Edita      : Umaru Aliyu