1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tsugune ta ki karewa a Masar

December 24, 2013

Wani harin Bom da aka kai a kasar Masar ya yi sanadiyyar mutuwar a kalla mutane 14 tare kuma da jikkata wasu da dama.

https://p.dw.com/p/1AgEA
Ägypten, Dakahlija, Mansura, Anschlag, Autobombe
Hoto: Reuters

Kakakin gwamnatin wucin gadi ta kasar Sherief Shawki, ya dora alhakin harin da aka kai da mota a ofishin 'yan sanda na kasar kan kungiyar 'yan uwa Musulmi dake ci gaba da zanga-zanagar nuna adawa da kifar da gwamnatin Mohamed Morsi.

Mahukuntan kasar ta Masar dai sun bayyana harin da aka kai da sanyin safiyar wannan Talatar (24.12.13) da wani yunkuri na dakile kokarin gwamnati na komawa kan turbar dimokaradiyya a kasar. Rahotannin sun bayyana cewa sa'oi kalilan bayan kai harin, Firaministan kasar Hazem Beblawi ya sanya kungiyar 'yan uwa Musulmi dake goyon bayan hambararren tsohon shugaban kasar Mohamed Morsi a sahun kungiyoyin ta'adda.

Mawallafiya: Lateefa Mustapha Ja'afar
Edita: Saleh Umar Saleh