1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Trump da shirin sasanta Isra'ila da Falasdinu

Binta Aliyu Zurmi
January 28, 2020

Trump ya sanar da shirinsa na zaman lafiya a yankin Gabas ta Tsakiya wanda ya bukaci samar da kasar Falasdinu wadda cibiyarta za ta kasance a gabashin Birnin Kudus.

https://p.dw.com/p/3WwW5
USA Washington Weißes Haus | Benjamin Netanjahu, Israel & Donald Trump, Präsident | Friedensplan Nahost
Hoto: picture-alliance/AP Photo/A. Brandon

Shugaban Amirka Donald Trump ya gabatar da shirinsa da aka dade ana jira na wanzar da  zaman lafiya a tsakanin Israila da Falasdinawa yayin da ya karbi bakuncin Firamininsta Benjamin Netanyahu da jagoran adawa Benny Gantz a fadar White House.

Shirin ya bai wa Falasdinawa damammaki fiye da yadda aka yi tsammani. Wannnan dai abu ne da ake ganin ya kawo karshen rade radin cewa gwamnatin Shugaba Trump na shirin yin hakan ne ba tare da samun amincewar shugabannin Falasdinawa ba.

Trump ya bukaci Falasdinawan su amince da shirin, amma tuni suka ci alwashin yin fatali da shi. Amirka dai na kan bakarta na bai wa Isra'ila karfin ikon yankuna da dama na gabar yammacin kogin Jordan.