1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Trump da Erdogan sun tattauna kan Libiya

Zulaiha Abubakar
January 16, 2020

Shugabannin kasashen Turkiyya Recep Tayyip erdogan da na Amirka Donald Trump sun tattauna ta wayar tarho kan hanyoyin maido da zaman lafiya kasar Libiya, gabanin taron tattauna da zai gudana a Berlin.

https://p.dw.com/p/3WH4y
US-TURKEY-DIPLOMACY
Hoto: Getty Images/AFP/J. Watson

A ranar Lahadi mai zuwa shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel z ata karbi bakuncin shugabannin kasashen Turkiyya da Rasha da Amirka da Birtaniya da Faransa da kuma Italiya domin lalubo mafita a rikicin kasar Libiya, bayan kin amincewa da yarjejeniyar tsagaita wuta da bangarorin da ke yaki da juna a Libiyan suka yi bayan kammala taron sulhu a Rasha a ranar Litinin din data gabata.

Yayin tattaunawar shugabannin kasashen Turkiyar da Amirka sun tabo yanayin da kasar Siriya ke ciki da zanga-zanga a Iran bayan rikitowar jirgin kasar Ukraine.