1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tawagar Kungiyar Kasashen Larabawa na ci gaba da ziyara a Siriya

December 28, 2011

Gwamnatin Siriya ta yi belin firisinoni kimanin 800 a yayin da tawagar Kungiyar Kasashen Larabawa ke cigaba da ziyara a kasar

https://p.dw.com/p/13b6A
epa03043901 A handout photo released by the official Syrian Arab News Agency (SANA), shows Syrians waving their national flags holding pictures depicting Syrian President Bashar Assad during a rally condemning the two terrorists blast of the 23 December, in Damascus, Syria on 27 December 2011. Arab League monitors on 27 December visited the Syrian city of Homs, which has been at the heart of anti-government protests and where according to activists around 60 people have been killed by shelling from the army in the past 24 hours. The visit is part of a deal between Damascus and the Arab League to end a ten month crackdown on anti-government protesters by the government, led by President Bashar al-Assad. Over 5,000 people have been killed in the clashes between the army, protesters and army defectors, according to UN estimate. EPA/SANA HANDOUT EDITORIAL USE ONLY/NO SALES +++(c) dpa - Bildfunk+++
Zanga-zanga a SiriyaHoto: picture-alliance/dpa

Duk da kasancewar tawagar sa ido ta kasashen Larabawa a kasar Siriya, har yanzu ana ci gaba da aranga tsakanin masu zanga-zanga da dakarun gwamnati.

Saidai a yau hukumomin Siriya sun yi belin mutane kusan 800 daga kurkuku.

Belin firisinoni da janye tankokin yaki daga cikin garurawan da sojoji suka mamaye na daga bukatocin da kungiyar kasashen larabawa ta gabatarwa shugaba Bashar Al-Asad.

A cewar Komitin Koli mai adawa da gwamnatin Siriya, sallamar mutanen 800 na matsasyin wani salo na yaudara da gwamnatin ta bullo da shi, domin karkata hankalin tawagar dake ke ziyara a Siriya.

A wani labarin kuma,ministan harkokin wajen Jamus Guido Westerwelle, ya kiri jikadan kasar Siriya a birnin Berlin domin ya amsa tambayoyi game da harin da wasu mutane su ka kai wa Ferhad Ahma,wani dan adawar kasar Siriya a birnin Berlin.

A wani abu mai kama da jan kunne,Westerewelle ya sanar da jikadan na Siriya cewar, Jamus ba zata amincewa ba, a taka hakin duk wani mahaluki dake cikin kasar.

A daren Litinin ne zuwa safiyar Talata, wasu mutane biyu da ba a tantance ba, suka kai hari gidan Ferhad Ahma, dake birnin Berlin, inda har suka ji masa raunuka.

Ferhad Ahma memba ne a komitin koli da 'yan adawar Siriya suka girka, domin jagorantar gwagwarmayar neman sauyi.

Mawallafi: Yahouza Sadissou Madobi

Edita: Ahmad Tijani Lawal