1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tashin hankalin Siriya na ƙara yin muni

July 9, 2012

Shugaba Bashar al-Assad ya zargi Amirka da ƙasashen yammancin duniya da rura wutar rikicin ƙasarsa

https://p.dw.com/p/15Trh
HANDOUT - Ein undatiertes Handoutfoto, das von der ARD-Anstalt SWR am Sonntag (08.07.12) zur Verfügung gestellt wurde, zur Berichterstattung über die Sendung «Weltspiegel», zeigt - im Exklusiv-Gespräch im Weltspiegel - Jürgen Todenhöfer (l), Publizist und Nahost-Kenner, der den syrischen Präsidenten Baschar al-Assad befragt. Die Sendung wird Sonntag um 19.20 Uhr im Ersten Programm (ARD) ausgestrahlt werden. ACHTUNG - Verwendung nur im engen inhaltlichen, redaktionellen Zusammenhang mit genannter WDR-Sendung bei Nennung der Quelle: «Bild: SWR» +++(c) dpa - Bildfunk+++
Hoto: SWR

Manzon musamman na Majalisar Ɗinkin Duniya, Kofi Ananan ya isa a birnin Damaskas inda zai gana da shugaba Bashar al-Assad domin samun mafita ga tashin hankalin da a ka ƙwashe kusan watanni 16 ana faman yi.Mista Annan wanda wannan ita ce ziyara ta ukku da ya ke kaiwa a ƙasar ta Siriya ba tare da samun nasara ba akan yunƙurinsa na diflomasiya na warware taƙaddamar ya na tare ne da rakiyar ƙungiyar ƙasashen Larabawa.

A cikin wata hira da tashar telbijan ta DW shugaba Bashar al-Assad ya soki Amirka da ƙasashen yammancin duniya da ƙara rura wutar rikicin, sannan ya ce kasarsa a shirye take ta tattuana. Ya ce: " kofofinmu buɗe suke ga duk wata ƙasa da ke neman taimaka wa a samu sulhu. Rahotanni daga Siriyar na cewar mutane aƙalla 99 suka mutu a ƙarshen mako a garruruwa daban-daban a cikin yamutsin.

Mawallafi: Abdourahamane Hassane
Edita : Halima Balaraba Abbas