1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Taron hukumar IAEA

March 7, 2006
https://p.dw.com/p/Bv5g

ela, yayi barazanar hallaka, saban Praministan Palestinu Ismael Haniyeh.

A Kasar Kenya, dubunan mutane, sun shirya zanga zanga, domin maida martani, ga harin da dakarun gwamnati su ka kaiwa wata kafar sadarwa mai zaman kanta, a makon da ya gabata.

Yanzu ga labaran dalla dalla………………………………

Hukumar yaƙi da yaɗuwar makaman nuklea ta Majalisar Ɗinkin Dunia, ta shiga yini na 2, a zaman taron, da ta buɗa jiya a birnin Vienna.

Wakilan ƙasashe 35, membobin wannan hukuma, na tantana batutuwa daban daban, da su ka haɗa da matsalar makaman nukleyar ƙasar Iran, da ake ta famar kai ruwa rana, a kan ta, a halin yanzu.

A cikin wannan taro, wakilan za su binciki, rahotanin da shugaban hukumar, Mohamed El Baradei, ya tattaro, a game da rikicin na Iran, sannan su yanke shawara, a kan wajibcin gurfanar da Iran gaban komitin Sulhu na Majalisar Ɗinki Dunia, ko kuma akassin haka.

A nasu gefe, hukumomin Iran, sun jaddada matsayin su, na babu gudu babu ja da baya, a game da aniyar da su ka ɗauka, da sarrafa makamashin nuklea, domin ƙara samun wadatar hasken wurtar lantarki, a faɗin ƙasa.

Sannan sunyi, hannun ka mai sanda, ga Amurika ,da ke barazanar kai hari ga Iran, da cewar dakarun ƙasar, a shire su ke, su fuskanci ƙalubale ta ko wace hanya.