1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Afirka da Turai na Taro

Suleiman Babayo LMJ
February 17, 2022

An fara taron tsakanin shugabannin kasashen Afirka da na Turai karkashin kungiyoyin nahiiyoyin a birnin Brussels da ke kasar Beljiyam.

https://p.dw.com/p/47AtM
Frankreich |  Emmanuel Macron mit Senegals Präsident Sall und Ghanas Präsident Akufo-Addo
Hoto: Ludovic Marin/AFP/Getty Images

Shugaban kasashen Turai na nahiyar Afirka sun hadu a wannan Alhamis domin fara taron kwanaki biyu na kungiyoyin nahiyoyin biyu, kan bunkasa zuba jari, yayin da Turai ke fuskantar gasa daga kasashen China da Rasha a nahiyar Afirka. An dan samu tsamin danganta tsakanin Turai da Afirka bisa samar da riga-kafin annaobar cutar coronavirus zuwa nahiyar Afirka gami da fadada da ake samu na sojojin haya na Rasha a rikice-rikicen da suke faruwa a nahiyar Afirka.

Shugaba Macky Sall na Senegal wanda yake rike da shugabancin karba-karba na shugabannin kasashen Afirka ya ce burin Afirka yayin taron da Turai shi ne fadada dangantaka tsakanin bangarorin biyu ta yadda Afirka za ta iya samun ci-gaban zamani da take bukata.