1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Magan ce matsalar 'yan gudun hijira Afirka zuwa Turai.

Kamaluddeen SaniNovember 11, 2015

Shugabanin kasashen kungiyar Tarayyar Turai na shirin tallafawa nahiyar Afirka da Euro Biliyan 3.6 a kokarin su na taimakawa wajen magance matsalar kwararar 'yan gudun hijira zuwa Turai.

https://p.dw.com/p/1H3l6
Entwicklungstage in Brüssel
Hoto: picture-alliance/dpa

Taron dai zai karbi bakuncin sama da shugabanni 50 da suka fito daga tarayyar Turai da Afirka a wani yunkurin baya-bayan nan da Turai take na duba daukar matakan magance kwararar 'yan gudun hijirah daga Afirka zuwa Turai.

Kazalika tallafin kudaden daTarayyar Turan za ta bayar za a yi amfani ne dasu wajen daukar matakan karfafa harkokin tattalin arzikin masu son neman mafaka ne zuwa Turai.

A yayin da yake magana da manema labarai kwamishinan harkokin 'yan gudun hijirar na kungiyar EU Dimitris Avramopoulos yace kasashen Turan za su ci gaba da yau kaka danganta da kasashen Afirka don kare lafiyar 'yan gudun hijirar, gami da dakile safarar su zuwa Turai.