1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

John Magufuli zai sake tsayawa takara

Abdoulaye Mamane Amadou
June 17, 2020

Shugaba John Magufuli na Tanzaniya, ya bayyana cewa zai sake tsayawa takara a manyan zabukan kasar da za a gudanar ciki har da na shugaban kasa a watan Oktoban da ke tafe.

https://p.dw.com/p/3dvNF
Präsident John Magufuli aus Tansania
Hoto: Getty Images/AFP/M. Spatari

Duk da zargin rashin 'yanci da walwala da aka zargi shugaban da aikatawa a wa'adin mulkinsa na farko, Shugaba Magufuli ya sake samun sahalewar jam'iyyarsa ta CCM, wacce ya ce ta zabeshi don ci gaba da aiwatar da ayyukansa na gari a wani sabon wa'adi na biyu na mulki.

'Yan adawa sun sha caccakar gwamnatin John Magufuli, bisa rashin iya jagoranci, sai dai ana hasashen cewa za a gudanar da zaben ne a yayin da kasar ke cikin wani yanayi na fuskantar annobar corona, duk da yake rahotanni na nuni da cewar shugaban na sako-sako da ita.