1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan za ta katse hulɗa da Sudan ta Kudu

June 8, 2013

Shugaban Sudan Umar Hassan Al Bashir ya ba da ummarnin da a dakatar da fiton man Fetur na Sudan ta Kudu zuwa tashoshin jiragen ruwa na ƙasashen waje.

https://p.dw.com/p/18mHn
An oil worker walks in an oil production facility in Paloch in South Sudan's Upper Nile state, on May 5, 2013, where South Sudan's Minister for Petroleum and Mining Stephen Dhieu Dau is on visit to resume oil production in the region after a 16-month hiatus, which may bring hope to the war-ravaged new nation. Crude oil accounted for 98 percent of the impoverished but resource-rich nation's revenue until a dispute with former civil war foe Sudan led to a shutdown in oil production in January 2012. AFP PHOTO / Hannah McNeish (Photo credit should read HANNAH MCNEISH/AFP/Getty Images)
Hoto: Hannah Mcneish/AFP/Getty Images

Sanarwa wace Gidan Rediyon na ƙasar ya bayyana ta zo ne makonnin biyu, bayan da aka sake cimma yarjejeniyar fiton da aka dakatar a can baya tsakanin ƙasashen biyu.

Sanarwa ta ce shugaban ya bai wa ministan harkokin man fetur na ƙasar ummarnin dakatar da fiton daga bakin gobe Lahadi. Ko da shi ke ba a bayyana dalilan ɗaukar matakin ba, amma da allama ba zai rasa nasaba ba ,da goyon bayan da Sudan ɗin ke zargin Sudan ta Kudu na bayar wa ga 'yan tawayen Kordofan ta Kudu. Wanda tun da fari shugaban ya yi barazanar cewar zai dakatar da fiton inda hukumomin Juba suka ci-gaba da ba su goyon baya.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Usman Shehu Usman