1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan ta janye daga yankin Abyei

June 2, 2012

Sudan Ta Kudu ta buƙaci sanyawa Sudan takunkumi duk da janyewar da ta yi daga yankin Abyei.

https://p.dw.com/p/156wW
Sudanese President Omar al-Bashir attends the opening of the second Arab-African summit in the coastal town of Sirte, Libya, 10 October 2010. According to media reports, the summit will hone in on key issues surrounding Palestinian-Israeli negotiations and the upcoming South Sudan referendum scheduled for January 2011, which could decide the future of a unified Sudan. This year's summit, organised by both the African Union and the Arab League, is the first for over 30 years. EPA/SABRI ELMEHEDWI +++(c) dpa - Bildfunk+++ usage Germany only, Verwendung nur in Deutschland
Shugaban Sudan Omar al-BashirHoto: picture-alliance/dpa

Jami'ai daga rundunar sojin Sudan sun sanar da cewar Sudan ɗin ta janye jami'an 'yan sandanta daga yankin Abyei mai arziƙin man fetur da take taƙaddamar mallakarsa tare da Sudan Ta Kudu. Tuni dama Sudan Ta Kudu wadda ita ma ke da'awar mallakar yankin na Abyei ta janye dakarunta daga yankin. Tunda farko dai Sudan ta ce za ta ci gaba da jibge rundunar 'yan sanda ta musamman mai ƙunshje da dakaru 169 a yankin na Abyei domin bada kariya ga rijiyoyin man fetur na Difra, amma ta janye wannan ƙudirin a wannan Jumma'ar sakamakon matsin lamba daga al'ummomin ƙasa da ƙasa. A yanzu dai akwai wata rundunar kiyaye zaman lafiya ta Majalisar Ɗinkin Duniya mai ƙunshe da dakarun ƙasar Ethiopia 3,800 dake kula da sha'anin tsaro a yankin. Hakanan a Jumm'ar nan ce Sudan Ta Kudu ta gabatarwa kwamitin sulhun Majalisar Ɗinkin Duniya buƙatar sanyawa Sudan takunkumi bisa zargin da tace na jefa bama-bamai a yankunan ta.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Usman Shehu Usman