1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Sudan za su mika mulki bayan cimma matsaya

Ramatu Garba Baba
November 21, 2021

Rahotannin sun tabbatar da shirin sojojin da suka kwace iko a Sudan na mayar da hambararren Firaiminista Abdallah Hamdok kan mukaminsa bayan cimma wata yarjejeniya.

https://p.dw.com/p/43Iwh
Sudan Khartum | Proteste gegen Militärregierung
Hoto: AFP/Getty Images

A wata sanarwar da ta fito yanzu ta hannun Fadlallah Burma Nasir, wanda shi ne shugaban jam'iyyar Umma,  ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, Hamdok zai dawo mukaminsa zai kuma kafa majalisar ministoci mai zaman kanta nan bada jimawa ba.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, a wannan Lahadin, za a saki duk wadanda ake tsare da su kamar yadda aka cimma a karkashin yarjejeniyar da aka kulla a yammancin jiya Asabar.  Masu zanga-zangar sun tsaya kai da fata na ganin an maido da gwamnatin riko ta farar hula da Hamdok ke jagoranta bayan da Janar Abdel Fattah al-Burhane ya jagoranci juyin mulki tare da nada kansa a matsayin shugaban majalisar rikon kwarya ta kasar ya hambarar.