1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sudan: Fada ya barke da sojoji a Khartoum

Abdullahi Tanko Bala
April 15, 2023

Fada ya barke a birnin Khartoum tsakanin sojojin gwamnatin Sudan da kungiyar tsaro ta kar ta kwana mai karfin tasiri RSF

https://p.dw.com/p/4Q8Vf
Hayaki ya turnuke a filin jirgin saman Kahrtoum
Hayaki ya turnuke a filin jirgin saman KahrtoumHoto: AFP

Rundunar tsaron ta RSF ta yi ikrarin karbe iko da fadar shugaban kasa da kuma filin jirgin sama a wani abu mai kama da yunkurin juyin mulki.

Sai dai sojin Sudan karkashin jagorancin Janar Abdel Fattah al Burhan a cikin wata sanarwa ta ce ta karbe ragamar shugabancin kungiyar ta RSF ba tare da wata turjiya ba. 

Sojojin sama na Sudan sun kai farmaki sansanonin RSF inda suka fattake su a cewar sanarwar rundunar sojin.

Rundunar sojin Sudan din dai ta baiyana dakarun na RSF a matsayin runduna ta yan tawaye.