1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sosomin lafawar kura a Siriya

January 2, 2012

Bisa ga dukkan alamu an kama hanyar samar da zaman lafiya a Siriya sakamakon janyewar dakarun gwamnatin daga unguwannin da ake zanga-zanga

https://p.dw.com/p/13d2r
In this photo taken on Wednesday Dec. 21, 2011, anti-Syrian regime protesters shout slogans during a demonstration in the Baba Amr area, in Homs province, Syria. Arab League monitors kicked off their one month mission in Syria with a visit on Tuesday, Dec. 27, 2011 to Homs, the first time Syria has allowed outside monitors to the city at the heart of the anti-government uprising. Several from the team of 12 stayed in the city overnight, and the team continued to work in Homs on Wednesday. The monitors are expected to visit Hama, Idlib and Daraa on Thursday, Dec. 29, all centers of the uprising. (Foto:AP/dapd)
'Yan zanga-zangar nuna adawa da Shugaba AssadHoto: dapd

Kungiyar kasashen Larabawa ta ba da sanarwar janye dakarun gwamnati daga unguwanin da ake gudanar da zanga-zanga a cikinsu a kasar Siriya inda hakan ke ma'anar sosomin tafarkin samar da zaman lafiya. A cikin jawabin da ya yi a birnin Alkahira na kasar Masar, babban sakataren kungiyar Nabil al Arabi ya ce yanzu sojoji sun janye zuwa wajen birane. To sai dai har yanzu akwai 'yan bindiga da ke ci gaba da yin barazana.

Da farko dai an soki tawagar 'yan sa ido ta kungiyar kasashen Larabawa a dangane da tashin hankalin da aka ci gaba da fuskanta a daiden lokacin da take ziyara a kasar -dalilin da sa ya wani komiti na masu fada a ji a kungiyar ya bukaci dakatar da aikin tawagar ba da bata wani lokaci ba. Komitin mashawartan kungiyar mai mambobi 88 ya ce ci gaba da fuskantar tashin hankali a ma lokacin da tawagar ke ziyara a Siriya na maanar ba da goyon baya ga shugaba Bashar Al Assad.

Mawallafiya: Halima Balaraba Abbas
Edita: Mohammad Nasiru Awal