1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sojojin Somaliya sun shiga garin Kismayu

October 1, 2012

Ɗaruruwan dakarun gwamnatin Somaliya sun kutsa garin Kismayu mai tashar jirgin ruwa a kudancin ƙasar.

https://p.dw.com/p/16IG4
Hoto: picture-alliance/ dpa

A wannan Litinin an girke ɗaruruwan sojojin gwamnatin Somaliya da mayaƙan sojojin sa kai dake mara musu baya a tsakiyar garin Kismayu dake zama sansanin sojojin sa kan ƙungiyar Al-Shabaab. Mohamud Farah kakakin rundunar sojin gwamnati a yankunan kudancin Juba ya faɗa wa kamfanin dillancin labarun Reuters cewa an aike da dakaru 450 domin sintiri a garin, sannan za a tsugunar da su a shelkwatar 'yan sanda. Da farko dai an jiyo kakakin sojin na cewa dakarun tarayyar Afirka da na gwamnatin Somaliya ba za su yi gaggawar shiga garin ba a daidai lokacin da ake fama da zaman ɗarɗar game da hare haren ɗaukar fansa da suka addabi garin mai tashar jirgin ruwa. Kawo yanzu ba a sani ba ko dakarun ƙasar Kenya dake faɗa ƙarƙashin tutar rundunar kiyaye zaman lafiya ta ƙungiyar tarayyar Afirka, su ma sun shiga tsakiyar garin. A ranar Juma'a mayaƙan al-Shabaab suka tsere daga Kismayu biyo bayan wani farmakin ba zata da sojojin ruwa da na sama da kuma na ƙasa suka kai.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Saleh Umar Saleh