1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana zargin juyin mulki a Burkina Faso

Binta Aliyu Zurmi
January 24, 2022

Sojoji da ke adawa da gwamnati a Burkina Faso sun tsare shugaban kasa Roch Marc Christain Kabore da wasu ministocinsa a wani sansaninsu da ke Ouagadougou bayan wani bore da ya auku a kasar.

https://p.dw.com/p/460He
Hoto: facebook.com/Presidence.bf

Al'umma a burkina Faso na cikin rudani bayan da aka jiyo karar harbe-harbe a kusa da fadar shugaban kasar Roch Marc Christain Kabore da ke Ouagadougou, yayin da wasu rahotanni ke ayyana hakan da zargin juyin mulki a kasar da ke fama da rikicin ta'addanci, ya zuwa wannan lokaci sojoji sun tabbatar da tsare shugaban kasa da shi da wasu ministocinsa. Wannan dai na zuwa ne bayan wani bore da sojojin suka yi na bukatar canza wasu shugabanninsu da ma neman karin kayayyakin yaki da mayakan jihadi da ke gwagwarmaya da makamai a kasar. A jiya Lahadi ne wani gungun matasa da ke bore a akan halin da kasar ke ciki suka cin nawa shelkwatar jam'iyyar Shugaba Kabore wuta. Ayyukan ta'addanci a kasar ta Burkina ya yi sanadin mutuwar rayukan mutane da dama tare ma da raba wasu da matsugunnansu.