1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Sojojin Najeriya sun musanta kai harin ramuwar gayya Delta

March 18, 2024

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ba wa dakarun sojin kasar umarnin bankado wadanda ke da hannu a kashe sojoji 16 a jihar Delta da ke da arzikin man fetur tare da bayyana kisan a matsayin dabbanci da ba za su lamunta ba.

https://p.dw.com/p/4drht
Wani atisayen sojin Najeriya
Wani atisayen sojin Najeriya Hoto: AFP/Getty Images

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito cewa sojojin Najeriya na ci gaba da kona dukkan gidaje da sauran gine-ginen da ke yankin tun bayan da wasu fusatattun matasa suka hallaka sojojin kasar kimanin 16 a karshen mako, wadanda ke aikin wanzar da zaman lafiya a yankin tun bayan barkewar rikicin kabilanci da kuma na mallakar kasa a yankin Okuoma da ke jihar Delta.

Karin bayani: Martani mai zafi kan kisan sojoji a Delta 

Babban hafsan hafsoshin Najeriya, Janar Christopher Musa ya musanta kai harin ramuwar gayya yankin, inda ya shaida wa Reuters cewa kokarin bankado wadanda suka gudanar da aika-aikar suke ba wai maida martani ba.