1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Siriya: Turkiyya na shirin yi wa Afrin kawanya

Salissou Boukari MNA
March 10, 2018

Dakarun kasar Turkiyya da ke samun goyon bayan wani bangare na 'yan tawayen Siriya, sun matso daf da birnin Afrin, inda suke a kimanin kilomita hudu da birnin da ke a matsayin cibiya ta Kurdawan kungiyar YPG.

https://p.dw.com/p/2u5PJ
Syrien FSA Operation Olivenzweig Afrin
Dakarun Sojojin TurkiyyaHoto: picture alliance/AA/H. Nasir

Tun daga ranar 20 ga watan Janairu ne sojojin na Turkiyya suka ayyana kai hare-hare ta sama a yankin na Afrin da ke arewa maso yammacin kasar Siriya.

A halin yanzu dai sojojin na Turkiyya na kokarin yi wa birnin na Afrin kawanya, bayan da suke rike da kashi 60 cikin 100 na yankin a cewar Rami Abdel Rahmane shugaban kungiyar kare hakin bil-Adama ta OSDH a kasar ta Siriya.

Hare-haren na Turkiyya ya yi sanadiyyar mutuwar sama da mayaka 370 na Kurdawan na YPG da kuma mayakan da ke mara musu baya sama da 340 a cewar wannan majiya. Sai dai rundunar sojojin kasar ta Turkiyya ta ce sojojinta 42 suka mutu a wannan yaki.