1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Siriya ta tsunduma cikin yaki: inji Assad

June 27, 2012

Shugaba Assad na Siriya yace babu makawa a yanzu kam kasarsa ta tsunduma cikin yaki gadan gadan.

https://p.dw.com/p/15MS4
Syria's President Bashar al-Assad speaks to the new government in Damascus in this handout photo distributed by Syrian News Agency (SANA) June 26, 2012. Al-Assad issued a decree to form a new government on Saturday, shaking up many cabinet posts but keeping the heads of the interior, defence and foreign ministries, state television reported. REUTERS/SANA/Handout (SYRIA - Tags: POLITICS) FOR EDITORIAL USE ONLY. NOT FOR SALE FOR MARKETING OR ADVERTISING CAMPAIGNS. THIS IMAGE HAS BEEN SUPPLIED BY A THIRD PARTY. IT IS DISTRIBUTED, EXACTLY AS RECEIVED BY REUTERS, AS A SERVICE TO CLIENTS
Hoto: REUTERS

Shugaban kasar Syria Bashar al-Assad ya ayyana cewa kasarsa na cikin yaki tsundum bayan watanni 15 tana fama da rigingimu na cikin gida. Da yake jawabi wajen rantsar da sabbin yan majalisar gudanarwar gwamnatinsa a jiya, shugaba Assad ya ce gwamnati za ta yi amfani da dukkan matakan da suka dace wajen samun nasara a wannan tarzoma.

" Yace Syria ta sami kanta a cikin yaki, a saboda haka idan mutum ya kasance a cikin yanayi na yaki, to kuwa zai iya yin amfani da matakan da suka dace ta kowace hanya domin samun nasara".

A can makobciyarta kasar Turkiya Firaminista Racep Tayyip Erdogan ya yi barazanar daukar matakin soji akan Damascus matukar sojojin Syria suka kusanci kan iyakar Turkiya. Gargadin ya zo ne bayan harbo jirgin Turkiyan da Syria ta yi a makon da ya gabata.

Mawallafi: Abdullahi Tanko Bala
Edita: Umaru Aliyu