1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Farar hula na cigaba da tserewa daga yankin Idlib

Zulaiha Abubakar
January 17, 2020

Shugabar hukumar kare hakkin 'dan Adam ta Majalisar Dinkin Duniya Michelle Bachelet ta bukaci kawo karshen rikici a yankin Idlib na Siriya, bayan ta bayyana takaicin yadda mahukunta suka gaza kare rayuwar fararen hula.

https://p.dw.com/p/3WMUU
Schweiz Bachelet kritisiert Vorgehen von Polizei und Armee in Bolivien
Hoto: AFP/F. Coffrini

Bachelet ta kuma kara da yin Allah wadai da yadda bangarorin da ke rikici da juna a Siriya suke luguden wuta ta sama a yankunan da fararen hular ke zaune, a jiya Alhamis wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewar daga watan Disambar bara zuwa yanzu akalla al'ummar Siriya da yawansu ya kusan dubu dari uku da hamsin, mafiya yawansu mata da kananan yara sun tsere daga yankin na Idlib zuwa makotan yankuna a iyakokin kasar da Turkiyya inda suke rayuwa cikin ragaita.