1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugabar taimakon jin kai ta Majalisar Dinkin Duniya ta isa Siriya

March 7, 2012

Valerie Amos shugabar hukumar taimakon jin kai ta Majalisar Dinkin Duniya ta sauka Siriya domin tattaunawa.

https://p.dw.com/p/14GVd
epa03135412 A handout picture released by Syrian Arab news agency (SANA), shows Syrian Foreign Minister Walid Mualem (R) meeting with UN humanitarian chief Valerie Amos (L) in Damascus, Syria, 07 March 2012. Amos arrived in Damascus earlier in the day for a two days and will visit Homs, said a U.N. spokesman in Syria, Khalid al-Masry. EPA/SANA HANDOUT BEST QUALITY AVAILABLE HANDOUT EDITORIAL USE ONLY/NO SALES
Valerie Amos da Walid al-MoualemHoto: picture-alliance/dpa

Shugabar hukumar taimakon jin kai ta Majalisar Dinkin Duniya Valerie Amos ta isa kasar Siriya a ranar Larabar nan domin yin kira ga gwamnatin kasar ta bada damar shigar da kayan agaji a biranen da tarzoma ta yiwa kaca-kaca. Valerie Amos wadda ta sauka birnin Damascus za ta tattauna da shugaba Bashar al-Assad. A ganawar da ta yi da Ministan harkokin wajen Siriyan Walid al-Mualem ya tabbatar mata cewa gwamnati za ta bada cikakken hadin kai.

A jiya manyan kasashe biyar masu kujarar dundundun a kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya sun gudanar da taro domin karin matsin lamba akan gwamnatin Siriya ta kawo karshen luguden wutar da take yi.

A waje guda kuma jakadan kasar Sin na shirin tattauna wani jadawali mai kudirori shida da Ministan harkokin wajen Siriya Walid Mu'alem domin kawo karshen rikicin. Ita ma kasar Rasha ta sake nanata kira ga gwamnati da yan tawayen Siriyan su gaggauta dakatar da fada.

Mawallafi: Abdullahi Tanko Bala
Edita: Saleh Umar Saleh