1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar da Mali da Burkina Faso na taro kan makomarsu

July 6, 2024

Shugaban majalisar mulkin soji na Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani ya karbi bakuncin takwarorinsa na kasashen Mali da Burkina Faso a babban birnin kasar Yamai.

https://p.dw.com/p/4hxUF
Shugaba  Assimi Goïta na Mali da Abdourahamane Tiani na Nijar da Ibrahim Traoré na Burkina Faso
Shugaba Assimi Goïta na Mali da Abdourahamane Tiani na Nijar da Ibrahim Traoré na Burkina FasoHoto: Francis Kokoroko/REUTERS; ORTN - Télé Sahel/AFP/Getty; Mikhail Metzel/TASS/picture alliance

 

A karon farko, kasashen Nijar da Mali da kuma Burkina Faso da suka kwace mulki da tsinin bindiga daga hannun farar hula na gudanar da taron koli a karkashin kungiyar kawance ta AES.

Shugabannin sun kafa kungiyar kawancen yankin Sahel wato AES  bayan fice wa daga ECOWAS  sakamakon dakatar da su daga harkokin kungiyar. Dama dai kasashen sun yanke alaka da tsohuwar uwargijiyarsu Faransa, inda suka karkata alakarsu da kasar Rasha.

Karin bayani: Shugaban Nijar na ziyarar aiki a Mali da Burkina Faso

Fadar shugaban kasa ta Burkina Faso ta ce, batun yaki da ta'addanci da kuma karfafa hadin gwiwa a tsakanin kasashen su ne batutuwan da za su mamaye zauren tattaunawarsu. Kasashen Nijar da Mali da kuma Burkina Faso sun sha fama da matsalolin kungiyoyin da ke gwagwarmaya da makamai a kan iyakarsu wanda ya yi sanadin rayukan dakarun soji da kuma fararen hula da dama.

A gefe guda, shugabannin kungiyar ECOWAS za su gudanar da taron koli a Najeriya a ranar Lahadi.