A cikin shirin za a ji cewa al'umomi daga sassa dabam-daban na Najeriya na mayar da martani kan wani kazamin hari da 'yan bindiga suka kai wa jirgin kasa mai jigila daga Abuja zuwa Kaduna. A Jamhuriyar Nijar kuwa wata kungiar da ke fafutikar kare muhalli ce ta shirya taron wayar da kan al'umma irin illolin da ke tattare da gurtaba muhalli a yankin Agadez.