matan kan yi korafin cewa ana mantawa da su musamman ta fuskacin shan romon dimukuradiyya. A Najeriya sau tari 'yan siyasa idan zabe ya gabato su kan shiga kauyuka su rinka rabawa mata atamfofi da sabulai da makamantansu. Su kan shiga gida-gida domin neman kuri'u na matan, sai dai da zarar sun samu nasara, su kan manta da dukkanin alkawuran da suka yi wa matan. Ba ya ga haka, matan kan koka da cewa ba ma a basu damarmakin da dokokin kasa da kasa da ma kundin tsarin mulkin Najeriyar ya ba su, wato adadin kason da aka amince a baiwa mata a mukamai na siyasa da ma na tafiyar da harkokin gwamnati. Sau da dama matan kan koka cewa a kan yi amfani da su a lokutan yakin neman zabe kana a yi musu abin nan da Malam Bahaushe ke cewa an ci moriyar ganga an yasar da kaurenta, kana ba ma a barinsu su taka rawar azo a gani idan batun tsayawa takara ya zo, ma'ana ba a barinsu su fito takarkaru a mukamai da ban-daban ko kuma idan ma har an bar sun a kan tsula kudi na ban mamaki, wanda hakan kan hana su samun damar tsayawa takarar.