1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shari'ar shugaban Kenya a gaban kotun ICC

November 26, 2013

Kotun ICC ta ce tilas ne shugaba Kenyatta ya halarci zaman kotu muddin dai bai sami hanzarin kotu ba.

https://p.dw.com/p/1AP8K
Kenya's President Uhuru Kenyatta makes his statement to the nation at the State House in Nairobi on September 22, 2013, following the overwhelming numbers of casualties from the Westgate mall shooting in the Kenyan capital. Kenyan President Uhuru Kenyatta said Sunday a nephew and his fiancee were among the 59 people confirmed killed in an ongoing siege in an upmarket shopping mall by Somali militants. AFP PHOTO / JOHN MUCHUCHA (Photo credit should read John Muchucha/AFP/Getty Images)
Hoto: John Muchucha/AFP/Getty Images

Kotun hukunta manyan laifukan yaki da ke birnin The Hague na kasar Holland ta sanar da cewar, tilas ne shugaba Uhuru Kenyatta na kasar Kenya ya rinka halartar zaman sauraron shari'ar da ta shafeshi a gaban kotun, muddin dai ba ta bashi damar kauracewa zaman ba, bayan ya nemi izini. Kotun ta yanke wannan shawarar ce yayin zaman da alkalan suka yi a wannan Talatar, a wani abin da ake ganin zai kara dagula dangantakar da dama ta yi tsami a tsakanin hukumomin kasar ta Kenya da kuma na gwamnatocin kasar Afirka - a hannu guda, kana da kotun a daya hannun.

Shugaba Uhuru Kenyatta da kuma mataimakinsa William Ruto dai, na fuskantar tuhumar da ta shafi aikata manyan laifuka a kan bil'Adama saboda rawar da suka taka a rigingimun da suka biyo bayan zabukan kasar a shekara ta 2007, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar kimanin mutane dubu daya da 200. Dama dai alkalan da ke sauraren shari'ar manyan jami'an biyu, na amsa bukatun da suke gabatar musu na rashin halartar zaman kotun, domin gudanar da wasu manyan ayyukan da suka shafi ofisoshinsu a cikin gida da kuma wajen kasar.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Mouhamadou Awal Balarabe