1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mahukuntan Saudiyya sun kare mace mace saboda tsananin zafi

Zainab Mohammed Abubakar
June 21, 2024

Wani babban jami’in Saudiyya ya kare tsarin tafiyar da aikin hajjin da masarautar ta yi, bayan da kasashe daban-daban suka bayar da rahoton mutuwar sama da mutum dubu saboda tsananin zafi.

https://p.dw.com/p/4hNN1
Hoto: Rafiq Maqbool/AP Photo/picture alliance

Ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewar, masarautar ta yi iyakar kokarinta, amma akwai kuskure a bangaren mutanen da ba su yi la'akari da hadarin da ke tattare da yanayin ba, a martanin farko da ke fitowa daga bangare gwamnati kan mace-macen.

Kididdigar da AFP ya gabatar a wannan Juma'a, wanda ya hada bayanan hukuma da rahotanni daga jami'an diflomasiyya da ke da hannu a martanin, ya ce adadin wadanda suka mutu ya kai 1,126, fiye da rabinsu daga kasar Masar.

Gwamnatin Saudiyya ta tabbatar da mutuwar mutane 577 a cikin kwanaki biyun farko masu tsanani na aikin hajji: Ranar Asabar lokacin da mahajjata suka taru na tsawon sa'o'i na addu'o'i a cikin rana mai zafi a dutsen Arafat, da kuma Lahadi, a lokacin da suka yi "jifan shaidan" na farko a Mina.

A baya dai mahukuntan Saudiyya sun ce mahajjata miliyan 1.8 ne suka halarta a bana, kamar na bara, kuma miliyan 1.6 sun fito ne daga kasashen waje.