1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Saudiyya ba za ta daidaita huldarta da Isra'ila ba

Mohammad Nasiru Awal AH
August 19, 2020

Cimma yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin Isra'ila da Falasdinawa na zama sharadin kulla hulda tsakanin Saudiyya da Isra'ila.

https://p.dw.com/p/3hD2T
Ministan harkokin wajen Saudiyya Yerima Faisal bin Farhan Al Saud da takwaransa na Jamus Heiko Maas a birnin Berlin
Ministan harkokin wajen Saudiyya Yerima Faisal bin Farhan Al Saud da takwaransa na Jamus Heiko Maas a birnin BerlinHoto: picture-alliance/dpa/J. MacDougall

Sabanin kasar Hadaddiyar Daular Laraba, kasar Saudiyya ta ce ba za ta daidaita dangantakarta da kasar Isra'ila ba, matsayawar ba ta cimma yarjejeniyar zaman lafiya da Falasdinu ba.

Ministan harkokin wajen Saudiyya Yerima Faisal bin Farhan ya fadi haka a wannan Laraba yayin wata ziyara da ya kai a birnin Berlin fadar gwamnatin Jamus.

Ya ce dole zaman lafiya tsakanin Isra'ila da Falasdinu ya zama abin da kasashen duniya za su aminta da shi. Ya ce idan aka cimma wannan to komai ma mai yiwuwa ne.

A makon da ya gabata ne Isra'ila da Hadaddiyar Daular Larabawa suka sanar da kulla huldar diplomasiyya tsakaninsu. Daular Larabawa dai ta zama kasar Larabawa ta uku bayan kasashen Masar da Jordan da ta kulla huldar diplomasiyya da Isra'ila.