1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sahel: Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadi kan tallafi

October 19, 2020

Majalisar Dinkin Duniya, ta yi fatan taron kasashen da za su hadu don samar da kudaden agaza wa kasashen Sahel zai dubi musabbabin matsaloli ba kudaden kadai ba.

https://p.dw.com/p/3k7kz
Niger Armee | bewaffnete Truppe
Hoto: AFP/S. Ag Anara

Shugaban hukumar samar da agaji ta MDD, Mark Lowcock, ya ce dala biliyan guda da kasashen Denmark da Jamus da Tarayyar Turai da ma ita kanta Majalisar Dinkin Duniyar za su samar na da amfani matuka, amma kasashen na fama da rashin gwamnatoci na gari.

Kasashen na yankin Sahel da ake batu a kan su dai su ne Burkina Faso da Mali da kuma jamhuriyar Nijar.  

Haka nan baya ga batun rashin gwamnatoci a kasashen, Majalisar Dinkin Duniyar ta ce akwai matsalar yawan haihuwa babu tanadi da kuma sauyin yanayi.