1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabuwar makoma ga Jamus a yankin Sahel

Zainab Mohammed Abubakar
April 13, 2022

Ministar harkokin wajen Jamus Annalena Baerbock na ziyara mai wahala a Afirka. Ko har yanzu manufar rundunar sojin Jamus ta Bundeswehr na da wata makoma a Mali ko kuwa komawa Nijar ita ce mafita? 

https://p.dw.com/p/49tYH
Mali | Ziyarar ministar harkokin wajen Jamus Annalena Baerbock
Hoto: Florian Gaertner/photothek/picture alliance

Kasashen Afirka guda biyu ne ministar harkokin wajen Jamus Annalena Baebock za ta yada Zango a yankin yammacin Afirka. Mali da kuma janhuriyar Nijar. Kasashen biyu na fama da matsalolin tsaro. Za ta gana da shugabannin gwamnati a biranen Bamako da Niamey, tare da kai wa sojojin kasa da kasa na MINUSMA da EUTM ziyara.

Makomar rundunar sojin Jamus ta Bundeswehr a Malin na daga cikin muhimman batutuwa da za ta tattauna, kasancewa wa'adinsu a Mali na karewa a watan Mayu. An samu koma bayan danganta tsakanin gwamnatin mulkin sojin Mali da tarayyar Turai a watannin baya bayan nan, sakamakon ci gaba da dage lokutan mayar da kasar kan tafarkin dimukuradiyya da kuma alakar da ke tsakaninsu da sojojin Rasha.

Ziyarar ministar harkokin wajen Jamus Baerbock a Mali
Hoto: Kay Nietfeld/dpa/picture alliance

Tun a tsakiyar watan Maris ne dai Faransa ta sanar da janye dakrunta da ke yaki da masu tada kayar bayan na Mali. Yanzu kuma ana cigaba da mahawara a nan Jamus dangane da ko akwai bukatar sojojin Jamus din su ci gaba da zama a Mali, wadanda ke kasar tun shekara ta 2013 inda suke aikin bada horo ga jami'an tsaron Malin. Ulf Laessing  kwararre ne kan yankin Sahel a gidauniyar Konrad Adenauer.

"Hakika ya dace mu tattauna kan tsawon lokacin da muke son ci gaba da zama a Mali, ko manufofinmu  na aiki, ko me za mu iya ingantawa, amma zan yi gargadi game da janyewar ba zato ba tsammani, kamar yadda muka yi a Afganistan. Janyewar za ta kara tsananta matsalolin tsaro a Mali kuma ya baiwa Rasha dama."

Ministar harkokin waje Baerbock yayin ziyararta a Mali
Hoto: picture alliance/dpa

To sai dai duk da wannan damuwa, a ranar Litinin kungiyar tarayyar Turai ta dakatar da aikin bayar da horo a Mali. Bayan ganawarsa da ministocin harkokin wajen Turan a Brussel, jami'in kula da harkokin kasashen ketare na EU Josep Borrell ya ce, wannan matakin kadai ya haifar da illa ga rundunar sojin wannan kasa ta Afirka. A hirasa da tashar DW mai sharhi kan Nijar Seidick Abba ya ce akwai bukatar la'akari da wasu bangarori.

"Ba za a iya yakin da sojoji kadai ba. Akwai bukatar saka hannun jari wajen inganta rayuwar jama'a da makomarsu, misali a fannin horar da matasa sana'o'i. Ba wai kawai a tsaya ga sayen jirage masu saukar ungulu na yaki ko kara yawan sojoji a cikin rundunar ba. Bugu da kari dole ne a koma ga tushen matsalar tare da kawar da wuraren ta'addanci a yankin Sahel. A wannan fanni ne kasa kamar Jamus za ta iya taimaka wa Nijar."

Akwai sojojin Jamus 300 a bangaren rundunar Turai da ke horar da sojojin Mali da ake kira EUTM a takaice. Kazalika ta na da wasu jami'an soji 1,000 a bangaren shirin kiyaye zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya na MINUSMA. Kuma wa'adin zaman rundunonin biyu a Mali, zai kare nan da makonni, idan har majalisar dokoki ta Bundestag ta amince.