1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabuwar gwamnatin Masar

August 1, 2012

Hisham Kandil ya bayyana sunayen membobin Majalisar Ministocin da ya girka a Masar

https://p.dw.com/p/15hjQ
In this Wednesday, April 4, 2012 photo former Egyptian minister of water resources and irrigation in the outgoing, military-appointed government, Hesham Kandil poses for a portrait in Cairo, Egypt. On Tuesday, July 24, 2012, Egyptian President Mohammed Morsi, of the Muslim Brotherhood, named the young, U.S. -educated Kandil as the prime minister designate and tasked him with putting together a new administration, nearly a month after Morsi was sworn in as Egypt's first freely elected civilian president. (Foto:AP/dapd)
Firaministan Masar Hisham KandilHoto: dapd/DW

Fiye da wata guda bayan rantsar da Mohammad Mursi a matsayin shugaban ƙasar Masar, a yau Laraba Firaministan da ya naɗa Hisham Kandil, ya baiyana sunayen majalisar ministocin ƙasar.

Daga jerin ministocin gwamnatin dake barin gado, ƙalilan suka yi nasara yin tazarce.

Ministocin da suka samu nasara ci gaba da aiki, sun haɗa da Ministan kuɗi Momtaz al-Said, da kuma ministan harakokin waje Mohammad Kamel.

A lokacin da shugaba Mohammad Mursi ya naɗa Firaminista a watan da ya gabata,ya umurce shi ya fi bada fifiko ga ƙurewa a wurin zaɓen ministoci, ba tare da la'akari da ɓangarancin siyasa, addini ko na ƙabila ba.

Mawallafi:Yahouza Sadissou Madobi
Edita: Umaru Aliyu