1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabani tsakanin Amirka da China kan Chen Guangcheng

May 4, 2012

Dan gwagwarmayar hakki na China ya baiyana fatan samun damar kaura zuwa Amirka

https://p.dw.com/p/14pka
Hoto: AP

Dan gwagwarmayar  kare hakkin jama'a na kasar China, Chen Guangcheng, wanda kuma makaho ne, ranar Alhamis, lokacin  tattaunawa ta wayar tarho da yan majalisar dokokin Amerika, ya nemi kasar ta bashi mafakar siyasa. Yace ina son zuwa Amerika, inda zan huta, hankalina yakwanta, inji, lokacin zantawa da yan majalisar  na Amerika daga gadon asibiti, inda yake kwance a birnin Peking. Chen an kai shi asibitin ne bayan da a wani yanayi mai  ban-mamaki, ya tsere daga ofishin jakadancin Amerika, inda yake karkashin daurin talala. Hakan ya kawo wani sabon sabani a dangantaka tsakanin Amerika da kasar ta China. 

A ranar Alhamis din Chen  ya sami damar magana ta mintoci da dama ta wayar tafi-da-gidanka da yan majalisar  dokokin Amirka a Washington daga gadon asibitin sa a Paking, inda  aka sami mai fassara  tsakanin su a lokacin wayar.

Ina son saduwa da Hilary Clinton, inji  dan gwagwarmayar na kasar China da yake  baiyana rokon sa ga yan majalisar da suka saurare shi lokacin wata muhawara da suka yi  game da kasarta China.

 Chen Guangchen ya baiyana fata mai karfi ta samun goyon baya daga sakatariyar harkokin wajen ta Amirka, kuma yace yana so  ido da ido ya godewa Hilary Clinton, wadda ma har ya zuwa ranar Jumma'a da safe ta kasance a birnin Peking tana shawarwari.

Chen yana son  saduwa da Clinton ne saboda  burin sa shine ya kasance shi da  yayan sa da matarsa su kasance  cikin jirgin dake dauke da sakatariyar harkokin wajen ta Amerika,  yadda  ba tare da wani jinkiri ba zasu fice daga China. Shi kansa  Bob Fu, da ya fassara maganganun da   Chen yayi da yan majalisar dokokin,  babban abokine  kuma makuncin   dan gwagwarmayar neman hakkin  jam'ar, kuma shine shugaban  kungiyar kare hakkin jama'a  mai suna ChinaAid mai mazaunin ta a Texas. Fu ya shaidawa majalisar dokokin ta Amirka irin abubuwan da  Chen ya sanar dashi cewar sun gudana a wannan mako a ofishin jakadancin na Amirka a Peking.

Hillary Clinton und Hu Jintao beim chinesisch-amerikanischen strategischen und wirtschaftlichen Dialog
Sakatariyar harkokin wajen Amirka Hilary Clindon tare da shugaban China Hu JintaoHoto: Reuters

Idan har baka  fice daga ofishin jakadancinmu ba, inji Amirkawan  a gaban Chen, to kuwa ba zaka sake samun wata dama ta ido hudu da matarka ba, ko yayanka biyu. Chen ya  shaida mani cewar a sakamakon wwannan barazana, ya tsinci kansa cikin wani halina kaka-ni-kayi, inji Fu, dake jawabi a gidan television na CNN, inda ya kuma kara da cewa: Chen ya kasance a wani hali na  tsaka-mai-wuya, bai kuma san abin da zai yi ba.

Kungiyar kare hakkin yan Adam  ta ChinaAid da shugaban ta Fu, sun zargi ofishin jakadancin Amirka a Peking da laifin matsa lamba da kuma baiwa dan gwagwarmayar na China damar fita daga ofishin na jakadanci. Fu yace babban kuskure ne  Chen bayan kwanaki shida kawai a nemi ya bar ofishin jakadancin. Da kamata yayi a bashi karin lokaci. Yanzu haka dai ana samun karuwar masu sukan manufofin Airka kan kasar ta China.  Mitt Romney abokin takarar  Barack Obama, ya zargi shugaban na Amirka mai ci da laifin  yiwa gwamnati a Peking sasauci fiye da kima.

US-Präsident Barack Obama
Shugaban Amirka Barack ObamaHoto: picture-alliance/dpa

Idan rahotanni game da  halayen  da ofishin jakadancin Amerika Peking ya nuna suka tabbata gaskiya,, to amma  wannan rana ta  zama mai  muni ga batun yanci.

A maida martani, kakakin Obama yace shugaban na Airka yana daukar matsalar ta Chen  da gaske matuka,  to sai dai baya son  bata zumunci da dangantaka a fannoni da dama dake tsakanin Amirka da kasar ta China.

Mawallafi: Umaru Aliyu
Edita: Zainab Mohammed Abubakar