1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rundunar sojin Nijar ta kashe jigo a kungiyar IS

June 23, 2024

Rundunar sojin Nijar ta sanar da cewa, ta kashe wani zarto a kungiyar IS a lokacin da ta kai samame a kasar da ke yammacin nahiyar Afirka.

https://p.dw.com/p/4hPPY
Rundunar sojin Nijar ta kashe jigo a kungiyar IS
Rundunar sojin Nijar ta kashe jigo a kungiyar ISHoto: ISSOUF SANOGO/AFP

Rundunar sojin Nijar ta ce ta samu nasarar kashe babban jigo a kungiyar ta IS, Abdoulaye Souleymane Idouwal tare da wasu 'yan ta'adda tara ne a yayin musayar wuta a yankin Tillaberi da ke kusa da iyakar kasar da kasashen Mali da kuma Burkina Faso. Rundunar ta kuma kara da cewa, ta kama wasu 'yan ta'addda 31 a lokacin, ta kuma lalata duk wata hanyar sufuri da kuma sadarwarsu.

Karin bayani:Sojojin Nijar sun halaka 'yan ta'adda a Tillabery 

Yankin Tilaberi dai ya sha fama da matsalar 'yan ta'adda inda gwamantin mulkin sojin kasar ke ci gaba da yakar mayakan Boko Haram da ISWAP a wasu sassan kasar.