1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin siyasa a Masar

Usman ShehuJuly 10, 2012

Ƙasar Masar ta fada a rikicin siyasa, inda shugaba Mursi ke takun saka da sojoji da alƙalai

https://p.dw.com/p/15UUL
Egypt's new President Mohamed Mursi (C) and Field Marshal Mohamed Tantawi (2nd L), head of Egypt's ruling Supreme Council of the Armed Forces (SCAF), stand at attention for the national anthem during a ceremony where the military handed over power to Mursi at a military base in Hikstep, east of Cairo, June 30, 2012. Mursi was sworn in on Saturday as Egypt's first Islamist, civilian and freely elected president, reaping the fruits of last year's revolt against Hosni Mubarak, although the military remains determined to call the shots. The military council that took over after Mubarak's overthrow on February 11, 2011, formally handed power to Mursi later in an elaborate ceremony at the desert army base outside Cairo. REUTERS/Mohamed Abd El Moaty/Egyptian Presidency/Handout (EGYPT - Tags: POLITICS ELECTIONS MILITARY) FOR EDITORIAL USE ONLY. NOT FOR SALE FOR MARKETING OR ADVERTISING CAMPAIGNS. THIS IMAGE HAS BEEN SUPPLIED BY A THIRD PARTY. IT IS DISTRIBUTED, EXACTLY AS RECEIVED BY REUTERS, AS A SERVICE TO CLIENTS
Shugaba Muhammed Mursi na kasar Masar a lokacin rantsuwar kama aikiHoto: Reuters

A yaune ake saran majalisar dokokin ƙasar Masar za ta koma zamanta, bayan da sabon shugaban ƙasar Muhammed Mursi ya yi watsi da hukuncin kutu, kana ya umarci majalisar da ta koma aikinta. To amma kotun tsarin mulkin ƙasar a jiya ya sake jadda matsayinsa, inda yace hukuncin da ya yanke na rusa majalisar na nan daram. Ƙungiyar alƙalan Masar ta baiwa shugaba Mursi wa'adin sa'o'i 36 da ya soke matakin na sa, ko kuma ya gamu da fishinsu, haka dai su ma sojojin da suka mulki ƙasar ta Masar kafin zaben Mursi, sun aika masa irin wannan gargadin. Manyan janar din sojan Masar sukace za su ci gaba da kare kundin tsarin mulkin ƙasar. A watan jiyane kotu ta soke halarcin majalisa, daga bisani sojojin suka rusata dungurungum.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Umaru Aliyu