1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikici ya barke a Masar

May 2, 2012

Akalla mutane 20 suka rasu bayan da wasu wadanda ba'a san ko su wanene ba suka afkawa gungun masu zanga zangar adawa da mulkin soji

https://p.dw.com/p/14oKM
epa02800597 An Egyptian returns a tear gas grenade to a police vehicle (background) as others stand nearby during clashes between protesters and police forces in Tahrir square, central Cairo, Egypt, 29 June 2011. According to local media reports, clashes had began earlier on 28 June outside the Interior Ministry between families whose relatives died during the January uprising and security forces and moved after that to the Tahrir square area. Reports added that more than 2500 protesters scuffled with the police using firebombs and rocks, Police used tear gas to disperse the protesters and the clashes are continuing. The reason for the violence were not immediately clear. EPA/Mohamed Omar +++(c) dpa - Bildfunk+++
Hoto: picture-alliance/dpa

Wasu mutane wadanda ba'a san ko su wanene ba dauke da sanduna da kulake sun afkawa ayarin mutanen da ke zanga zangar adawa da mahukuntan mulkin sojin a wajen ma'aikatar tsaro dake birnin Alkahira. Mutane akalla 20 aka bada rahoton sun rasu yayin arangamar wasu da dama kuma sun jikata. Tun a ranar Asabar din da wuce magoya bayan dan takarar jam'iyyar Salafiyya Hazem Abu Ismail suka yi gangamin zaman darsham na har sai baba ta gani, bayan da hukumar zabe ta haramtawa fittacen dan takararta tsayawa takara a zaben shugaban kasar da za'a yi nan gaba a cikin wannan watan. Jam'iyyar yan uwa musulmi wadda ke da kusan rabin wakilai a majalisar dokoki ta kauracewa taron da majalisar sojin kasar ta kira domin nuna bacin ranta ga wannan abin da ya faru. Shima a nasa bangaren dan takarar jam'iyyar ta Muslim Brothers Mohammed Mursi yace zai dakatar da yakin neman zabe na kwana biyu domin nuna juyayi ga mutanen suka rasu da kuma wadanda suka sami raunuka.

Mawallafi: Abdullahi Tanko Bala
Edita: Usman Shehu Usman