1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rasha ta karfafa kawance da Afirka

February 9, 2023

A cewar Ministan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov kasar Rasha za ta iya karfinta don ganin MDD ta cire takunkumin da ta aza wa kasar Sudan.

https://p.dw.com/p/4NJKD
Sudan Besuch Außenminister Russland Lawrow
Hoto: Palace Media Office/REUTERS

Ministan ya ce, kasar Rasha za ta iya karfinta don ganin MDD ta cire takunkumin da aka aza wa kasar Sudan. Sergei Lavrov ya bayyana haka a Khartoum babban birnin kasar Sudan, yayin ziyarar aiki ta kwanaki biyu da ya kai a Sudan. Ministan harkokin wajen Rasha a ziyarar tasa, ya kuma gana da shugaban kasar Sudan Abdel Fattah al-Burhan, inda suka tattauna kan mahimman batutuwa na kara karfafa hulda tsakanin kasashen biyu. Ziyarar kasar Sudan, ita ce kasa ta uku da Lavrov ya ziyarta a Afirka, bayan kasashen Mali da Murtaniya. Kasar Rasha dai na kara karfafa kusancinta da kasashen Afirka, yayin da kasashen Yamma ke gograrin maida ita saniyar ware, ko da a watan jiya ministan harkokin wajen na Rasha Sargei Lavrov ya ziyarce kasashen  Eritrea, Angola, Eswatini Afirka ta Kudu. A Watan Juli kuwa za a yi taron hadakar Rasha da kasashen Nahiyar Afirka.