PEN: Babu 'yanci ga kalmar
Kungiyar marubuta ta PEN tana tunatar da duniya marubuta da yan jarida da ake zalunta a fadin duniya. Cibiyar PEN ta Jamus tana fafutukar kwato 'yancin wadannan marubuta na musamman.
Philippines: Maria Ressa
Maria Ressa ita ce ta kafa 'Rappler' da ke yada labarai ta yanar gizo a Philippines. A baya can, ta yi aiki a matsayin mai ba da rahoto ga CNN. A Philippines, wanda ya lashe kyautar zaman lafiya ta Nobel ana daukar shi a matsayin wanda ta fi sukar shugaban kasar Rodrigo Duterte mai barin gado da kuma munanan manufofinsa na yaki da muggan kwayoyi. Gwamnati na kokarin daure Ressa da umarnin kotu.
Turkiyya: Selahattin Demirtas
Dan siyasan Turkiyya mai adawa Selahattin Demirtas ya fafata da Shugaba Erdogan a zabukan 2014 da 2018. Tun a watan Nuwamban 2016 ake tsare da shi a wani gidan yari mai cike da tsaro bisa zargin farfagandar ta'addanci. Kotun Turai na neman a sake shi. Turkiyya mamba a majalisar Turai ba ta mayar da martani ba. Yayin da yake kurkuku, Demirtas ya fara rubuta littafin yayin da yake zaman kaso.
China: Rahile Dawut
Kamar daruruwan 'yan Uighur masu ilimi, Rahile Dawut ta bace daga idon jama'a ba tare da wata alama ba a cikin 2017. A cewar Human Rights Watch, an kama fitacciyar masaniyar ilimin kabilar Xinjiang a lokacin wani farmaki da aka kai kan mawakan Uighur, malamai, da 'yan jarida. Ana kyautata zaton ana tsare da ita a wani sansanin horarwa. Cibiyar PEN ta Jamus na yi wa Rahile Dawut yakin samun 'yanci.
Yuganda: Kakwenza Rukirabashaija
Shari'arsa ta ba da haske game da halin da ake ciki na 'yancin fadin albarkacin baki a Yuganda - an sace mai sukar gwamnati na Afirka, marubuci kuma lauya Kakwenza Rukirabashaija tare da azabtar da shi a bara, saboda litattafai masu ban tsoro da kuma sakonnin tweeter na rashin mutuntawa. Da taimakon PEN ya yi nasarar tserewa zuwa kasar Jamus, inda yake samun kulawar lafiyarsa.
Vietnam: Pham Doan Trang
Zarge-zarge da dauri na siyasa - gwamnati ta kai hari kan mawallafiyar yanar gizo ta Vietnamese kuma 'yar jarida Pham Doan Trang, saboda yakin da take yi da lalata muhalli, tashin hankalin 'yan sanda da kuma zaluntar tsiraru. Kungiyoyin kare hakkin bil adama da gwamnatoci da dama na neman a sake ta bayan da aka yanke mata hukuncin daurin shekaru tara a gidan yari a shekarar 2021.
Turkiyya: Osman Kavala
Lokacin da mai yada al'adun Turkiyya Osman Kavala ya bace a bayan gidan yari bisa wasu tuhume-tuhume a watan Afrilun 2022, ba kungiyar PEN kadai ta yi zanga-zanga ba, ita ma Amnesty International ta yi kira da a saki Kavala. Majalisar Turai ta sha sukar yadda Turkiyya ta gaza yin biyayya ga yarjejeniyar Turai kan kare hakkin dan Adam.
Zimbabwe: Tsitsi Dangarembga
Tsitsi Dangarembga, marubuciya kuma mai shirya fina-finai, ta sake gurfana a gaban kotu a kasarta ta Zimbabwe, saboda zanga-zangar kin jinin gwamnati. Ana zarginta da tada zaune tsaye a cikin al'uma, rashin zaman lafiya da kuma son zuciya. Dangarembga ta sami lambar yabo ta zaman lafiya ta cinikin littattafan Jamus a shekarar 2021.