1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Nijar za ta dauki dubban matasa aikin soja

November 30, 2020

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta ce za ta rubanya yawan sojojinta da ke aiki a rundunar kasa. Ministan Tsaron kasar Issoufou Katambe ne ya sanar da haka ga 'yan majalisar kasar.

https://p.dw.com/p/3lzpP
Demokratische Republik Kongo Kinshasa | Nigerianischer Präsidenten Mahamadou Issoufou
Hoto: Presidence RDC/G. Kusema

Ministan ya ce a karkashin wannan sabon yunkurin Nijar za ta kara yawan adadin sojojinta zuwa akalla dakaru 50,000 ko ma fiye da haka a cikin tsukin shekaru biyar.

A jawabin nasa na karshen mako, Issoufou Katambe ya ce a halin da ake ciki Nijar na da sojojin kasa guda 25,000 kuma bisa kiyasunsu kasar na bukatar dakarun soji 150,000 domin su samu damar yakar 'yan ta'adda yadda ya kamata. 

Jamhuriyar Nijar dai na fuskantar kalubalen tsaro na mayakan tarzoma a yankin Diffa da ke makwabtaka da Najeriya, ga kuma rikicin da take yi da 'yan ta'adda da ke shigo mata ta kan iyakokinta da kasashen Mali da Burkina Faso.