Neman a bincike take yancin ɗan Adam a Masar
August 20, 2013Hukumar kula da kare yancin ɗan Adama ta MDD ta buƙaci hukumomi a ƙasar Masar da su bar jami'an ƙasa da ƙasa su shiga ƙasar, don gudanar da bincike bisa take yacin jama'a, yayin tarwaza masu adawa da juyin mulkin soji, wanda hukumomi a ƙasar ta Masar suka yi a makon jiya. Kakakin hukumar Liz Trossell, na mai cewa suna matsawa hukumomin Masar lamba da su bar tawagar kula da kare yancin ɗan Adam da ta ziyarci ƙasar. Tun dai a makon jiya shugaban humar Navi Pillay ta buƙaci da a bar masu bincike daga ƙasa da ƙasa, masu zaman kansu da su gudanar da bikicike kan yadda aka yi amfani da ƙarfi a rikicin na Masar.
A gefe guda shi ma Sakatare janar na MDD Ban Ki-moon ya yi mummunar suka bisa yadda sojojin na Masar suka tinkari siyasar ƙasar. Ban ki-moon yace a kaɗu da mutuwar 'yan Muslim Brotherhood 37 yayinda suke tsare a hannun jami'an tsaro. Kana ya soki kisan da aka yi wa 'yan sanda 25 a yankin Sinai.
A wani labarin da ya shafi rikicin siyasa: Hukumomi a ƙasar Masar sun tsare Mohamed Badie, jagoran addini na ƙungiyar Muslim Brotherhood, bisa tuhumar sa da hannu wajen kisan masu zanga-zanga a watan Juni.
Mawallafi: Usman Shehu Usman
Edita: Umaru Aliyu