1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

NATO ta nemi a bar Finland da Sweden zama mambobinta

Binta Aliyu Zurmi
February 28, 2023

Sakatare janar na kungiyar kawancen tsaro ta NATO Jens Stoltenberg ya yi kira ga kasashen Turkiyya da Hungary da cewar lokaci ya yi da za su sakar wa kasashen Finland da Sweden mara domin shiga kungiyar.

https://p.dw.com/p/4O4nY
NATO-Generalsekretär Jens Stoltenberg und Ministerpräsidentin Sanna Marin aus Finnland
Hoto: Heikki Saukkomaa/picture alliance/dpa/Lehtikuva

Jens Stoltenberg da ya yi wannan kira a birnin Helsinki na kasar Finland, ya ce yanzu ne dai-dai lokacin da ya kamata kasashen na Turkiyya da Hungary su sauko daga kujerar naki da suka dare domin ganin an sami maslaha a korafe-korafen da suke hana ruwa gudu.

Tun a watan Mayun shekarar da ta gabata ne bayan mamayar Rasha a Ukraine, kasashen biyu na Finland da Sweden a hukumance suka mika takardar neman shiga kungiyar tsaron, sai dai bukatun nasu ya ci karo da turjiya da yanzu haka ake fatan magance ta.


Stoltenberg ya ce duka kasashen biyu sun cika sharudan da aka cimma da Ankara, Sai dai a nata bangaren Ankara ta ce har yanzu Sweden ba ta kai ga cika wadannan sharuddan ba.


Ana dai ganin akwai alamun nasara a bangaren Turkiyya tun bayan sanarwar da ta yi na yiwuwar ci gaba da tattaunawa a ranar 9 ga watan Maris da za mu shiga.